
Jam’iyar LP ta zaɓi, Nenadi Usman a matsayin cikakkiyar shugabar jam’iyar.
An zaɓi Usman a ranar Talata a wurin babban taron jam’iyyar da aka gudanar a Umuahia babban birnin jihar Abia.
Jam’iyar ta kuma zaɓi wasu mambobinta da za su riƙe wasu ofisoshin jam’iyar na ƙasa.
A cikin waɗanda aka zaba akwai Iheanacho Obioma a matsayin sakataren jam’iyar na kasa,Niki Oriola mataimakin shugaban jam’iyar, da kuma Ken Asogwa da aka zaba a matsayin mai magana da yawun jam’iyar.
Sauran sun hada da Oluchi Oparah sakatariyar tsare-tsare ta kasa,Ansalem Eragbe sakataren kudi da kuma Hilda Dokubo a matsayin shugabar mata.
Da take magana bayan kammala taron ta mika godiyarta ga jam’iyar da kuma gwamnan jihar Abia, Alex Otti ta bayyana cewa za ta mayar da hankali wajen samar da haɗin kai, zaman lafiya da sulhu a jam’iyar gabanin zaɓen 2027.

