Nan gaba kaɗan zamu bayyana sunayen wasu manyan mutane dake da hannu a satar mai – Garba Shehu

Mai taimakawa shugaban kasa, Muhammad Buhari kan kafofin yada labarai, Mallam Garba Shehu ya ce nan bada jimawa gwamnatin tarayya za ta bayyana sunayen wasu manyan mutane dake da hannu a satan man ƙasar nan

Shehu ya ce a wani ɓangare na kawar da zagon kasa ga tattalin arzikin ƙasar nan da wasu mutanen ƙalilan masu haɗama suke yi jami’an tsaro sun kai farmaki kan wasu wurare da ake satar danyen mai.

Garba Shehu ya bayyana haka ne a cikin shirin Politics Today na gidan talabijin Trust TV ya kuma haskaka cewa akwai wasu jami’an tsaro da suke aikata wannan haramtaccen aiki.

Ya kara da cewa ana cigaba da daukar karin sababbin matakai domin shawo kan lamarin.

More News

Kotu Ta Hana PDP Cire Shugaban Riƙon Jam’iyar

Wata Babbar Kotun Tarayya dake Abuja ta hana jam'iyar PDP dakatar da Umar Damagum daga matsayinsa na shugaban riƙon jam'iyar. Mai Shari'a  Peter Lifu shi...

Tinubu Ya Dawo Abuja Daga Ziyarar Aiki Da Ya Kai  Saudiya da Nezaland

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya dawo Abuja bayan ziyarar aiki da ya kai ƙasashen Saudiya da Nezaland. A ranar 22 ga watan Afrilu ne...

CBN ya dakatar da kudirinsa na sa bankuna su riƙa cajar kwastomominsu

Babban bankin Najeriya ya umarci bankunan da su dakatar da cajin kudaden ajiya har zuwa ranar 30 ga Satumba, 2024.Babban bankin ya bayyana hakan...

Ƴansanda sun kama likitan bogi

Rundunar ‘yan sanda ta Zone 2, Onikan, Legas, ta kama wani likitan jabu mai shekaru 37, kuma ma’aikacin lafiya, tare da zargin amfani da...