Najeriya na fuskantar mummunan matsin tattalin arziki da ba ta taɓa fuskanta ba—Sanata Abdullahi

Shugaban kwamitin majalisar dattawa kan tsare-tsare da harkokin tattalin arziki, Yahaya Abdullahi, ya ce Najeriya na fuskantar matsalar tattalin arziki mafi muni a tarihin wanzuwarta.

Abdullahi, wanda ke wakiltar mazabar Kebbi ta Kudu a jihar Kebbi, ya bayyana hakan ne a taron kaddamar da kwamitin majalisar a ranar Laraba.

Wannan dai kamar yadda ya ce akwai bukatar majalisar ta yi mu’amala da bangaren zartarwa a wani yunkuri na sake farfado da tattalin arzikin kasar da kuma dawo da shi kan turba.

Abdullahi ya kuma bukaci kwamitocin tsare-tsare na kasa a cikin majalisar da majalisar dattawa da su yi duk mai yiwuwa a cikin shekaru hudu don cimma burin da aka tsara na juya tattalin arzikin kasar, tare da ba da shawara ga hukuma.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]