Mourinho na son Arsenal; Ibrahimovic zai zamansa a LA Galaxy

Emile Smith Rowe, Reece James, Harvey Elliott and Brandon Williams

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Tsohon kocin Manchester United da Chelsea Jose Mourinho na son komawa Ingila saboda yana son ci gaba da lashe manyan lambobin yabo na kwallon kafa da kungiya ta uku. (Sky Sports)

An ce Mourinho zai so ya karbi ragamar kungiyar Arsenal idan aka yi masa tayi. (ESPN)

Manchester City na son sake daukan Jadon Sancho daga Borussia Dortmund, amma dan wasan mai shekara 19 zai yi tsada matuka, inda ake hasashen zai kai fam miliyan 100. (Sport Bild, ta hannun Sport Witness)

Manajan LA Galaxy Dennis te Kloese na shirin ganawa da Zlatan Ibrahimovic, mai shekara 38, domin tattaunawa kan tsawaita zamansa a kungiyar. (ESPN)

Juventus ta shirya tsaf domin sayar da Mario Mandzukic mai shekara 33 ga Manchester United ko Sevilla a watan Janairu, amma tana bukatar fam miliyan 4.6. (Calciomercato, ta hannun Mirror)

Manchester City da Arsenal na rige-rigen sayen Isco dan wasa mai shekara 27, wanda dan wasan tsakiya na Real Madrid ne da kasar Sfaniya (Mundo Deportivo, via Manchester Evening News)

Dani Alves ya ce tilas Neymar – wanda dan wasan gaba na Paris St-Germain da Brazil ne – ya sauya halayyarsa idan yana son abokan wasansa su mutunta shi, kuma ya ce a yanzu yana da halin kananan yara ne. (Spor TV, ta hannun jaridar Independent)

Joao Pedro dan Brazil mai shekara 18 ya sami izinin yin aiki a Ingila,matakin da zai ba shi zarafin buga wasa da kungiyar Watford a watan Janairu mai zuwa. An sayo shi daga Fluminense ne kan fam miliyan 2 a watan Oktobar 2018, amma tun lokacin yake dakon takardun da za su ba shi damar yin aiki a Ingila. (Standard)

Liverpool, Borussia Dortmund da kuma Barcelona na son sayen Ferran Torres, dan wasan Sifaniya mai shekara 19 daga Valencia. (Sport Bild, via Metro)

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...