Mayakan Boko Haram sun kona gidaje a kauyen Mifa dake jihar Borno

Mayakan kungiyar Boko Haran sun kona gidaje da dama a Mifa wani kauye dake karamar hukumar Chibok ta jihar Borno.

Wani mazaunin kauyen ya fadawa jaridar The Cable cewa mayakan kungiyar masu yawa sun isa kauyen da misalin karfe 8 na dare inda suka shiga cinnawa gidaje wuta.

“Suna kona gidaje a yanzu da nake magana da kai da yawa daga cikinsu sun zo akan babura inda suka fara kai hari kan kauyen,” a cewar majiyar.

“Bamu san mutanen da abin ya shafa ba, sojoji sun iso yanzu duk da cewa yan ta’addar na cikin kauyukan.”

Ya cigaba da cewa da yawa daga mutanen kauyen sun tsere ya yin da harin ya jefa firgici a Chibok da makotan kananan hukumomi.

Mifa dake da tazarar kilomita 8 daga garin Chibok shine kauye na karshe da ya hada iyaka da dajin Sambisa mai ban tsoro.

More News

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Gidaje 8925

Gwamnatin tarayya ta ce ta fara raba gidaje 8925  ga mutanen da suka nema kuma suka cancanci a basu a faɗin ƙasa baki ɗaya...

Ƴan Bindiga A Zamfara Sun Kashe Sakataren Jam’iyar PDP

Wasu ƴan bindiga da ba a san ko suwaye ba sun kashe, Musa Ille  sakataren jam'iyar PDP na ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara. Zagazola...