Rahotanni na nuni da cewa mayakan Boko Haram sun kashe a kalla sojoji shida a wani hari kan sansanin sojoji dake kauyen Kareto a karamar hukumar Mobbar ta jihar Borno.
Yan ta’addar dake kan babura sun farma sansanin sojan da misalin karfe 7 na daren ranar Alhamis.
Harin na ranar Alhamis na zuwa ne kasa da wata guda bayan da mayakan suka kashe jami’an soja sama da 25 lokacin da suke tsaka da sauyawa mutanen wani kauye matsuguni.
Wata majiya ta fadawa jaridar The Cable cewa mayakan na Boko Haram sun shafe sama da sa’o’i uku suna musayar wuta da sojojin a harin na ranar Alhamis.
A cikin wadanda aka kashe a farmakin akwai kwamandan bataliya ta 158 ya yin da wasu daga cikin sojojin ba a san halin da suke ciki ba har ya zuwa lokacin da jaridar ke hada wannan rahoto.