Mayakan Boko Haram 78 Sun Mika Wuya Ga Sojoji

Sojojin rundunar sojan Najeriya sun kama wasu manyan jiga-jigan kungiyar yan ta’addar ISWAP.

Zagazola Makama dake ya wallafa bayanai kan sha’anin tsaro a yankin tafkin Chadi shi ne ya bayyana haka inda ya kara da cewa karin wasu mutane 60 aka kama tare da kwamandodin da ake zargin suma yan kungiyar ta ISWAP ne.

Har ila yau bayanan da ya wallafa ya nuna cewa mayakan Boko Haram 78 ne suka mika wuya sojojin shiya ta uku na rundunar kasa da kasa dake karamar hukumar Monguno.

Yan ta’addar sun mika wuya ne saboda farmakin da ake kai musu babu kakkautawa a maboyarsu.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) Æ™arÆ™ashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da Æ™arar da É—an majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]