Wasu mayakan da ake zaton yan kungiyar Boko Haram ne sun kashe manoma 15 a wasu hare-hare kan garuruwa biyu dake ƙaramar hukumar Jere ta jihar Borno.
A cewar Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan rikicin dake faruwa a yankin tafkin Chadi ya ce yan ta’addan sun kai hari kan Molai Kura da Molai- Gana.
Bayanan sun bayyana cewa ƴan ta’addar sun yanka manoman a gonarsu dake Molai a kusa da birnin Maiduguri.
” Aƙalla gawarwakin mutane 15 aka kwaso da safiyar nan, harin ya faru ne a ranar jiya (Alhamis) a cewar Bukar Ali Musty ɗaya daga cikin shugabannin yan bijilante.
“Manoma bakwai aka yanka suna aiki a gonarsu kuma maharan sun yanka wasu magidanta da basu ji ba su gani ba a gidajen su.”