Mayaƙan Boko Haram Sun Yanka Manoma 7 A Borno

Wasu mayakan da ake zaton yan kungiyar Boko Haram ne sun kashe manoma 15 a wasu hare-hare kan garuruwa biyu dake ƙaramar hukumar Jere ta jihar Borno.

A cewar Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan rikicin dake faruwa a yankin tafkin Chadi ya ce yan ta’addan sun kai hari kan Molai Kura da Molai- Gana.

Bayanan sun bayyana cewa ƴan ta’addar sun yanka manoman a gonarsu dake Molai a kusa da birnin Maiduguri.

” Aƙalla gawarwakin mutane 15 aka kwaso da safiyar nan, harin ya faru ne a ranar jiya (Alhamis) a cewar Bukar Ali Musty ɗaya daga cikin shugabannin yan bijilante.

“Manoma bakwai aka yanka suna aiki a gonarsu kuma maharan sun yanka wasu magidanta da basu ji ba su gani ba a gidajen su.”

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]