Mayaƙan Boko Haram Sun Yanka Manoma 7 A Borno

Wasu mayakan da ake zaton yan kungiyar Boko Haram ne sun kashe manoma 15 a wasu hare-hare kan garuruwa biyu dake ƙaramar hukumar Jere ta jihar Borno.

A cewar Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan rikicin dake faruwa a yankin tafkin Chadi ya ce yan ta’addan sun kai hari kan Molai Kura da Molai- Gana.

Bayanan sun bayyana cewa ƴan ta’addar sun yanka manoman a gonarsu dake Molai a kusa da birnin Maiduguri.

” Aƙalla gawarwakin mutane 15 aka kwaso da safiyar nan, harin ya faru ne a ranar jiya (Alhamis) a cewar Bukar Ali Musty ɗaya daga cikin shugabannin yan bijilante.

“Manoma bakwai aka yanka suna aiki a gonarsu kuma maharan sun yanka wasu magidanta da basu ji ba su gani ba a gidajen su.”

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa ɗaya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faɗa tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...