Manyan Jiragen Dakon Mai Na China Sun Ratsa Mashigar Hormuz



Wasu manyan jiragen dakon mai guda biyu na ƙasar China da ke ɗauke da ganga miliyan huɗu na ɗanyen mai sun ratsa mashigar Hormuz bayan sun shafe fiye da wata biyu suna jiran samun damar wucewa a yankin Tekun Fasha.

Bayanan kamfanonin Kepler da LSGA sun nuna cewa jiragen sun ɗauki ɗanyen man Gabas ta Tsakiya kafin su tsallaka wannan muhimmiyar hanyar ruwa a ranar Laraba.

Rahotanni sun ce a kwanakin baya jiragen ruwa kaɗan ne kawai suka rika amfani da mashigar Hormuz, sakamakon tashin hankali a yankin.

Sai dai nasarar da jiragen suka samu wajen wucewa tare da kalaman da Fadar White House ta yi kan yiwuwar zaman lafiya da Iran sun taimaka wajen rage farashin mai kaɗan.

A ranar Talata, shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa ana dab da cimma yarjejeniyar zaman lafiya da Iran, amma ya jaddada cewa duk wata yarjejeniya dole ne ta hana Iran mallakar makamin nukiliya.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]