Majalisar Kolin Harkokin Shari’ar Musulunci Ta Najeriya Ta Kalubalanci Shekau | VOA Hausa

A wani taron manema labarai da majalissar ta kira a Kaduna game da barazanar da Shekau ya yi a faifan bidiyon da ya fitar ta cewa lokaci ya yi da ya kamata Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya farga.

Daya daga cikin manyan malaman addinin Musulunci a Najeriya, Sheik Abdulwahab Abdullahi Mohammad, ya kalubalanci Shugaban Kungiyar ta Boko Haram Abubakar Shekau game da faifan bidiyon da ya fitar cewa har in ya cika jarumi, to ya fito yayi gaba-da-gaba da jami’an tsaro.

Wannan na zuwa a dai-dai lokacin da batun matsalar tsaro a Najeriya yake dada jan hankalin ‘yan kasa masamman ganin irin barazanar tsaron da aka fuskanta a kasar cikin wannan wata na Fabarairu.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]