Shugabannin ƙungiyar Jama’atu Izalatil Bid’a wa Iqamatis Sunna a Najeriya sun kama hanyar Jihar Kebbi da ke arewa maso yammacin kasar domin gabatar da jana’izar marigayi Sheikh Abubakar Giro Argungu.
Ƙungiyar ce ta bayyana haka cikin wata sanarwa a shafinta na Facebook.
Sanarwar ta ce: “Shugabanin IZALA sun tashi zuwa Birnin kebbi Domin halartan Janaza
“Shugaban JIBWIS Sheikh Bala Lau, da Shugaban Malamai Sheikh Dr. Jalo jalingo, sakataren kungiya Sheikh Kabiru Gombe, Sakataren tsare-tsare na majalisar agaji Sheikh Salisu Gombe. Sakataren marayu na kasa Alhaji Usman da sauran tawaga sun tashi zuwa Birnin kebbi domin samun janazan Sheikh Giro Argungu a garin Argungu. Allah ya sauke su lafiya. Amin”