Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna inda aka kashe wasu fasinjoji.

An bayyana wanda ya shirya harin da suna Ibrahim Abdullahi, wanda kuma aka fi sani da Mandi.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar, ACP Olumuyiwa Adejobi, wanda ya bayyana hakan a Kaduna a ranar Alhamis, ya kuma bayyana cewa wanda ake zargin yana cikin waɗanda suka sace daliban jami’ar Greenfield a shekarar 2021.

Adejobi ya kuma kara da cewa an kama shi da bindigun AK-47 guda 48, kuma ana ci gaba da kokarin gano wanda ya dauki nauyinsa da kuma sama masa da makamai.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]