Sarkin Musulmi ya ce an ga watan Ramadan a Najeriya

Mai Alfarma Sarkin Musulmi Sa’ad Abubakar, ya ayyana ranar Litinin 11 ga Maris, 2024, a matsayin 1 ga watan Ramadan.

Sanarwar ta zo ne biyo bayan ganin watan a sassa daban-daban na Najeriya a ranar Lahadi, wanda ke cika kwanaki 29 ga watan Sha’aban.

A wata sanarwa da ya fitar, Sultan Abubakar ya bayyana cewa an yanke wannan shawarar ne bisa rahotannin da shugabannin Musulmin kasar suka bayar na tabbatar da ganin watan.

Ya bukaci al’ummar Musulmi a Najeriya da su fara azumin ranar Litinin kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...