Majalisar Ɗinkin Duniya Ta Yi Gargaɗin Yunwa Ga Fiye Da Ƴan Najeriya Miliyan 30 A Bana

Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) ta yi gargaɗin cewa sama da ƴan Najeriya miliyan 30 na iya fuskantar matsalar yunwa a wannan shekara, sakamakon raguwar tallafin agaji da ake samu a faɗin duniya.

Hukumar ta bayyana cewa kusan yara miliyan uku na cikin barazanar rashin samun abinci mai gina jiki, lamarin da ke ƙara tsananta a jihohin Borno, Yobe da Adamawa, inda rikice-rikice suka yi kamari.

Kodinetan hukumar ba da agaji na MDD a Najeriya ya ce a halin yanzu ba za a iya dogaro da irin agajin da aka saba bayarwa a baya ba, saboda ƙarancin kuɗaɗe.

MDD ta ƙara da cewa za ta mai da hankali ne kan ayyukan ceton rai kawai, inda za ta ware kusan dala 500,000 domin tallafa wa mutane miliyan biyu da rabi a fadin ƙasar.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]