Maganin tari ya yi sanadin mutuwar yara 66 a Gambia

Akwai wani babur ɗin roba na wasa da aka ajiye a kusurwar gidan Mariam Kuyateh. Babur ɗin duk ya yi ƙura.

Asali babur É—in na É—anta ne mai watanni 20 da haihuwa mai suna Musa wanda ya rasu a watan Satumba.

Yana daga cikin yara 66 da suka rasu a Gambia sakamakon wani maganin tari da ake kyautata zaton sun sha wanda ya jawo musu ciwon ƙoda, kamar yadda Hukumar Lafiya ta Duniya ta bayyana.

Babu wani a gidan da ke taÉ“a babur É—in wasan na Musa – wanda wani abu ne da ke tuna abin da aka rasa.

Mahaifiyarsa mai shekara 30, wadda ke da Ć´aĆ´a huÉ—u, tana ta hawaye a yayin da take tuna abin da ya faru da É—anta.

A yayin da take zaune a gidanta a wajen birni mafi girma na Gambia wato Serrekunda, ta yi bayani dalla-dalla kan yadda ciwonsa ya fara a matsayin mura.

Bayan likita ya duba sa, sai mahaifinsa ya siyo masa maganin tari domin shawo kan matsalar.

“Ko da aka ba shi maganin, sai murar ta tsaya, amma kuma ta jawo wata matsala,” in ji Ms Kuyateh.

“ĆŠana ba ya iya fitsari.” in ji ta.

Sai ta koma asibiti inda aka yi wa Musa gwajin jini wanda gwajin ya nuna cewa yana ɗauke da zazzaɓin Maleriya.

Sai aka sake ba shi wani maganin har aka saka masa katata amma duk da haka ya kasa yin fitsarin.

A Ć™arshe dai sai dai aka yi wa Ć™aramin yaron tiyata. Babu wani ci gaban da aka samu. “Ya kasa warkewa, sai ya rasu.”

Asalin hoton, KUYATEH FAMILY

A farkon makon nan ne dai Hukumar Lafiya Ta Duniya ta fitar da wani gargaɗi kan wasu magunguna huɗu da ke da alaƙa da mace-mace a Gambia.

Magungunan sun haÉ—a da Promethazine Oral Solution da Kofexmalin Baby Cough Syrup da Makoff Baby Cough Syrup da Magrip N Cold Syrup waÉ—anda wani kamfanin Indiya ne yake haÉ—a su mai suna Maiden Pharmaceuticals.

Kamfanin dai ya gaza wurin tabbatar da ingancinsu, kamar yadda WHO ta bayyana.

Gwamnatin India dai ta soma bincike kan wannan lamari. Sai dai kamfanin bai ce komai ba ko da BBC ta so jin ta bakinsa. Jama’a da dama dai sun fusata kan lamarin da ya faru a Gambia.

Akwai mutane da dama da suke t akira ga ministan lafiya na ƙasar Dakta Ahmadou Lamin Samateh, tare da kama waɗanda suka shiga da magungunan a cikin ƙasar.

“Rai 66 na da yawa. A don haka muna buĆ™atar adalci, saboda waÉ—anda lamarin ya faru da su yara ne da ba su yi komai ba,” in ji Ms Kuyateh.

Asalin hoton, OMAR WALLY

Haka kuma akwai Aisha Ć´ar wata biyar wadda ita ma ta rasu sakamakon waÉ—annan magunguna.

Mahaifiyarta, Mariam Sisawo wata safiya ta gano cewa bayan Ć´arta ta sha maganin tarin, sai ta kasa yin fitsari.

Bayan ta je asibiti, sai aka shaida wa Mariam mai shekara 28 da cewa babu wani abu da ke damun Ć´arta.

Sai da mahaifiyar Aisha ta yi sawu biyu zuwa asibiti kafin aka mayar da ita zuwa wani asibiti da ke Banjul babban birnin ƙasar wanda ke da nisan kilomita 36 daga gidansu da ke Brikama, amma bayan an shafe kwana biyar ana ƙoƙarin yi mata magani, sai ta rasu.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...