Kungiyoyin ƙwadago za su fara yajin aiki ranar 8 ga watan Nuwamba kan cin zarafin Ajaero

Gamayyar kungiyoyin ƙwadago sun shirya shiga yajin aiki a ranar 8 ga watan Nuwamba kan yadda akaci zarafin shugaban kungiyar NLC, Kwamared Joe Ajaero.

Haɗakar kungiyar ƙwadago ta NLC da TUC sun gudanar da wani taron manema labarai a ranar Juma’a kan abin da ya faru a jihar Imo.

A ranar Laraba ne aka rawaito wasu jami’an tsaro sun yi awon gaba da Ajaero a hedikwatar kungiyar ta NLC dake Owerri.

Kungiyar NLC ta ce an lakada masa duka lokacin da yake hannun jami’an tsaro zargin da rundunar yan sandan jihar ta musalta inda ta ce wasu batagari ne suka dake shi amma jjami’an yan sandan su ka samu nasarar ceto shi.

A yayin ta taron manema labaran shugabannin ƙwadagon sun yi kira da a binciki kwamishinan yan sandan jihar Imo, Ahmad Barde kana a ɗauke shi daga jihar.

Shugabannin kungiyar sun kuma yi kira da a kama tare da hukunta Nwaneri Chinasa wani mai taimakawa gwamnan jihar da ake zargi jagoranta yan ta’addar da suka kai wa yan kungiyar da kuma ma’aikata farmaki.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]