Kasuwar cinikin ‘yan kwallo: Makomar Lingard, Haaland, Lukaku, Icardi, Ndidi, Felix, Ramsey, Pedri, da Januzaj

Wifred Ndidi

Newcastle ta tuntubi Manchester United, kan batun kai karshen cinikin Jesse Lingard a watan Janairu. (Sun)

Manchester United za ta nemi daya daga cikin yan gaba, Erling Haaland na Dortmund, ko Joao Felix na Atletico Madrid ko Timo Werner na Chelsea ko kuma matashin dan wasan Sweden Alexander Isak.

United na shirin sayen sabon dan gaba ne yayin da ake tunanin Edinson Cavani zai koma Barcelona. (Mail)

Dan wasan gaban Chelsea da Belgium Romelo Lukaku zai koma buga wasa a gasar Serie A ta Italiya kafin ya yi ritaya a cewar wakilinsa. (Tuttosport, via Goal)

Real Madrid ta nuna sha’awar sayen dan wasan Leicester da Najeriya Wilfred Ndidi, don maye gurbin Casemiro a tsakiya. (Naija)

Brighton na shirin kwace matashin dan wasan tsakiyar Poland Kacper Kozlowski da ke wasa a Pogon Szczecin. (Mail)

Kungiyoyi da yawa na son Erling Haaland

Barcelona za ta nemi Adnan Januzaj da zarar kwantiraginsa da Real Sociedad ya kare a karshen kaka. (Mail)

Haka ma Barcelona ta kyalla ido kan dan wasan gaban Manchester United Anthony Martial, watakila idan ta kasa samun Ferran Torres. (Sport – in Spanish)

Matar Mauro Icardi da wakilinsa na tattaunawa da PSG don duba yiwuwar komawar dan wasan Juventus a Italiya. (Fichajes – in Spanish)

A nan kuma dan wasan tsakiyar Sifaniya Pedri ya ce yana jin dadin zama a Barcelona duk da sha’awar da Manchester City ta nuna ta daukarsa. (Tuttosport – in Italian)

More News

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...