Jami’an tsaro sun samu nasarar halaka madugun ‘yan bindiga

Rundunar sojojin Najeriya bataliya ta 29, dake runduna ta 6 a birnin Fatakwal tare da wasu jami’an tsaron sa-kai ne suka fafata a wannan farmakin da ‘yan bindiga a yayin da suka yi kokarin satar mai.

Soja daya ya rasa ransa da wasu jami’an sa-kai su 2 sakamakon fito-na-fiton da jami’an tsaron suka yi da ‘yan bindigar. Ba tare da bata lokaci ba sansanonin tsaro daban daban a yankin suka kai agajin gaggawa wurin suka kuma bazama farautar ‘yan bindigar.

Jami’an tsaron sun sami nasarar cafke shugaban kungiyar da aka fi sani mai suna Nobel, har aka sami bindigogi daban daban a wurin sa amma shi ma daga bisani ya sheka lahira.

Shugaban runduna ta 6 ta sojin Najeriya, Manjo Janar Jamilu Sharham ya ce rundunarsa zata tabbatar da tsaro a wuraren da ake ayyukan hakar danyen mai a yankin.

Mai fashin baki akan lamuran tsaro, Ahmed Baba Tijjani Gamawa mai ritaya, ya ce kasancewar yanayin tsaro a yankin yanzu, akwai bukatar gwamnati, da gwamnan jihar Rivers, da jami’an tsaro su hau teburin sulhu ba tare da wata akida ta siyasa ba, don a kare rayukan jama’a da dukiyoyin su.

More News

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Gidaje 8925

Gwamnatin tarayya ta ce ta fara raba gidaje 8925  ga mutanen da suka nema kuma suka cancanci a basu a faɗin ƙasa baki ɗaya...

Ƴan Bindiga A Zamfara Sun Kashe Sakataren Jam’iyar PDP

Wasu ƴan bindiga da ba a san ko suwaye ba sun kashe, Musa Ille  sakataren jam'iyar PDP na ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara. Zagazola...