Jami’an tsaro sun ceto wasu ƴan NYSC da aka yi garkuwa da su

Rundunar sojojin Najeriya tare da hadin gwiwar ‘yan sanda sun ceto wasu mambobin yi wa kasa hidima, NYSC, da wasu ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a unguwar Yargoje da ke karamar hukumar Kankara a jihar Katsina.

Daraktan hulda da jama’a na rundunar, Brig.-Gen. Onyema Nwachukwu, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa ranar Juma’a a Abuja.

Mista Nwachukwu ya ce jajircewar da jami’an tsaro suka yi ne ya sa aka ceto wadanda aka sace tare da dawo da su lafiya a ranar Alhamis.

Ya ce barayin sun yi awon gaba da ‘yan kungiyar ne a lokacin da suke kan hanyar Edo zuwa jihar Katsina.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...