Hotunan bikin ranar demokradiyya a Najeriya

Najeriya ta yi bikin ranar Demokradiyya ran 12 ga Yuni, don tunawa da sahihin zabe na farko da aka fara yi a kasar ran 12 ga watan Yunin 1993, shekaru goma bayan mulkin soja.

Ga wasu daga cikin hotunan abubuwan da suka faru a lokacin bikin.

Hakkin mallakar hoto
FACEBOOK/BUHARI SALLAU

Shugaba Muhammadu Buhari da matarsa Aisha Buhari da Mataimakin Shugaban Farfesa Yemi Osinbajo da matarsa Dolapo Osinbajo da sabon Shugaban majalisar dattawa Sanata Ahmad Lawan da sauran manyan baki a wajen bikin.

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Daya daga cikin masu nishadantar da mutane a lokacin da take taka rawa a Dandalin Eagle Square da ke birnin Abuja.

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, a lokacin da ake tuka shi a mota inda ya ke duban masu faretin girmamawa a Dandalin Eagle Square.

Hakkin mallakar hoto
FACEBOOK/BUHARI SALLAU

Wasu daga cikin manyan baki da suka halarci taron bikin ranar demokradiyyar har da ‘yan kasashen waje.

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Faretin ‘yan sanda a lokacin bikin ranar demokradiyya a Abuja, babban birnin Najeriya.

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari yana gaisawa da shugaban Rwanda Paul Kagame a lokacin bikin. Daga bayansu kuma tsohon shugaban majalisar dattawan Najeriya ne Ken Nnamani da wasu manyan baki.

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Wasu sojoji suna fareti a gaban Shugaba Muhammadu Buhari yayin da shi kuma yake kallonsu a Dandalin Eagle Square a lokacin bikin.

Hakkin mallakar hoto
FACEBOOK/BUHARI SALLAU

Wasu ‘yan rawa suna nishadantar da ‘yan kallo a filin da aka gudanar da bikin a Abuja.

Hakkin mallakar hoto
FACEBOOK/BUHARI SALLAU

Shugaba Muhammadu Buhari a lokacin da yake jawabi a Dandalin Eagle Square.

Hakkin mallakar hoto
FACEBOOK/BUHARI SALLAU

Sufeto Janar na ‘yan sandan Najeriya, Mohammed Abubakar adamu yana sara wa Shugaba Muhammadu Buhari.

More News

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...

Manyan dillalan mai za su fitar da litar man fetur miliyan 300 a wannan makon

Ƙungiyar MEMAN ta manyan dillalan man fetur da dangoginsa ta ce mambobinta sun fara lodin mai har lita miliyan 300 a cikin makon nan...

Kotu ta É—aure mutumin sa ya yi sama-da-faÉ—i da kuÉ—in marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...