Gwamnatin Nijeriya Ta Kori Ma’aikatan Kamfanin Man Fetur Guda 850 Daga Aiki – AREWA News

Katafaren Kamfanin man Nijeriya na NNPC ya kori ma’aikatan sa 850 kuma akasarin su sun fito ne daga matatun man kasar da basa aiki yadda ya dace.

Sakataren kungiyar manyan ma’aikatan man kasar na PENGASSAN, Lumumba Okugbawa yace ma’aikatan da aka sallama sun kunshi kwararru da wadanda ba kwararru ba, tare da wadanda ke taimakawa wajen tafiyar da matatun man.

Kamfanin man NNPC bai yi bayani kan korar ma’aikatan ba, sai dai a makwannin da suka gabata, shugaban sa Mele Kyari ya bayyana damuwa kan asarar da kamfanin keyi wajen rashin ingantaccen aikin da matatun man kasar keyi, abinda ya sa Najeriya ta dogara da kasashen ketare domin samarwa al’ummar kasar tacaccen man fetur.

A watan Mayun da ya gabata, kamfanin NNPC yace yana da ma’aikata sama da 6,600 dake karbar albashi daga lalitar sa.

Nijeriya na daya daga cikin kasashen da suka dogara da albarkatun man fetur domin samun kudaden shigar da take amfani da su.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]