Gwamnatin Tarayya za ta fara rabawa ɗalibai bashi daga watan Satumba

Gwamnatin tarayya ta ce tana nan tana tsara hanyoyin da za abi domin raba bashin da za a bawa dalibai daga watan Satumba.

David Adejo, babban sakataren ma’aikatar ilimi shi ne ya sanar da haka lokacin da yake amsa tambayoyin yan jarida a Abuja.

A ranar Litinin ne shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya rattaba hannu kan dokar bawa dalibai bashin biyan kuɗin makaranta ba tare da sun biya kudin ruwa ba.

Adejo ya ce tsarin zai bawa ɗalibai yan Najeriya damar saukin samun ilimin gaba da sakandare ta hanyar cin bashi daga asusun Nigeria Education Loan Fund.

Babban sakataren ya ce sabuwar dokar za ta tabbatar kowane dan Najeriya ya samu damar samun ilimin gaba da sakandare.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]