Gwamnatin Tarayya za ta fara rabawa ɗalibai bashi daga watan Satumba

Gwamnatin tarayya ta ce tana nan tana tsara hanyoyin da za abi domin raba bashin da za a bawa dalibai daga watan Satumba.

David Adejo, babban sakataren ma’aikatar ilimi shi ne ya sanar da haka lokacin da yake amsa tambayoyin yan jarida a Abuja.

A ranar Litinin ne shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya rattaba hannu kan dokar bawa dalibai bashin biyan kuɗin makaranta ba tare da sun biya kudin ruwa ba.

Adejo ya ce tsarin zai bawa ɗalibai yan Najeriya damar saukin samun ilimin gaba da sakandare ta hanyar cin bashi daga asusun Nigeria Education Loan Fund.

Babban sakataren ya ce sabuwar dokar za ta tabbatar kowane dan Najeriya ya samu damar samun ilimin gaba da sakandare.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]