Gwamnatin tarayya ta ce tana nan tana tsara hanyoyin da za abi domin raba bashin da za a bawa dalibai daga watan Satumba.
David Adejo, babban sakataren ma’aikatar ilimi shi ne ya sanar da haka lokacin da yake amsa tambayoyin yan jarida a Abuja.
A ranar Litinin ne shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya rattaba hannu kan dokar bawa dalibai bashin biyan kuÉ—in makaranta ba tare da sun biya kudin ruwa ba.
Adejo ya ce tsarin zai bawa É—alibai yan Najeriya damar saukin samun ilimin gaba da sakandare ta hanyar cin bashi daga asusun Nigeria Education Loan Fund.
Babban sakataren ya ce sabuwar dokar za ta tabbatar kowane dan Najeriya ya samu damar samun ilimin gaba da sakandare.