Gwamnatin Imo Ta Hana Sauya Littattafai Akai-Akai A Makarantu



Gwamnatin jihar Imo ta haramta yawan sauya littattafan karatu a dukkan makarantu na gwamnati da masu zaman kansu a fadin jihar.

Haka kuma, ta dakatar da gudanar da bukukuwan yaye dalibai ga wasu matakai a tsarin karatu.

Kwamishinan Ilimin Firamare da Sakandare, Farfesa BTO Ikegwuoha, ya bayyana cewa an dauki wannan mataki ne domin rage wa iyaye da masu kula da yara nauyin kashe kudi a wannan lokaci na matsin tattalin arziki.

A cikin wata sanarwa da aka fitar, gwamnati ta umarci masu makarantu, shugabannin makarantu da malamai su bi wannan doka nan take, tare da gargadin cewa duk wanda ya saba zai fuskanci hukunci mai tsauri, har da soke lasisi.

More from this stream

Recomended