Gwamnan Jihar Taraba Ya Kai Ziyarar Farko Yankin Mambilla

Ita dai ziyarar jajen da gwamnan jihar Taraban ya kai yankin na Mambilla, na zuwa ne a dai-dai lokacin da aka shafe watanni goma sha bakwai da tashe-tashen hankulan, batun da wasu ke dangantawa da siyasa.

Ziyarar kwanaki uku da gwamnan ya kai ya gana da sarakuna da iyayen al’umma da ‘yan siyasa da kuma wasu daga cikin mutanen da lamarin ya shafa, ya kuma bukaci al’umomin yankin su hada kai da kuma yafewa juna.

Al’ummomin yankin sun yaba da wannan ziyarar, yayin da wasu ke suka.

To sai dai kuma tuni aka fara maida martani a ciki da wajen jihar. Gambo Dauda na cibiyar kare hakkin bil adama, ta ‘Centre For Human Rights Advocacy’ ya ce, abin mamaki ne duk da abubuwan da suka yi ta faruwa tun rikicin farko na watan Yunin shekarar 2017, har zuwa na watanin Maris da Afrilu da kuma na watan Mayun wannan shekarar, sai yanzu ne gwamnan jihar ke zuwa ziyarar jaje.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]