Gidan mari ne ya fi dacewa da dana saboda gagararsa, inji wata mata

Gidan Mari

Wata mata da ke birnin Kano wadda na daga cikin iyayen da ‘ya’yansu da aka kange a gidajen mari a fadin jihar, ta ce ba ta ji dadin yadda aka fasa gidajen marin ba.

Matar dai ta ce kasancewar dan nata ‘gagararre’ sannan kuma ita da mahifinsa duk sun tsufa ya sa ba ta fatan dan nata ya koma gida.

Gwamnatin jihar Kano dai ta bayar da umarni ga dukkan masu gidajen gidan mari da su kulle gidajen.

To sai dai da dama daga cikin mahaifan yaran ba su je sun dauki ‘ya’yan nasu ba saboda tsoron abin da ka je ya zo.

Ranar Alhamis din ne dai rana ta karshe da gwamnatin jihar ta Kano ta bayar domin kowane mahaifi ya dauke dansa daga gidan marin.

More News

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...

ĆŠan agajin Izala ya samu lambar yabo, kujerar hajji, kyautar mota bayan ya tsinci naira miliyan 100 ya mayar wa mai su

Salihu AbdulHadi Kankia, mamba ne na kungiyar agaji ta kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS), ya samu yabo da tukuicin mayar da...

Musulmi a Zaria sun yi taron addu’o’i saboda mummunan halin matsi da Najeriya ke ciki

Musulmi a garin Zaria na jihar Kaduna, sun gudanar da addu'a ta musamman domin neman taimakon Allah kan halin da 'yan Najeriya ke ciki...