Ganduje ya halarci bikin Mauludi a fadar Sarkin Kano

Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya jagoranci wata tawaga ta manyan jami’an gwamnati ya zuwa wurin Maulidi da aka gudanar a fadar mai martaba sarkin Kano Muhammad Sunusi II.

Shugaban darikar Kadiriya na Afrika ,Shekh Karibulla Nasiru Kabara shine yake jagoran maulidin da aka saba gudanarwa duk shekara.

Ziyarar ta daren Litinin na zuwa ne lokacin da gwamnan ke cigaba da fuskantar suka daga ciki da wajen jihar biyo bayan fefan bidiyon da wata jarida ta wallafa inda aka nuna shi yana karbar kudi daga hannun yan kwangila.

Mutane da dama dai nakira da gwamnan kan ya sauka daga kan mukaminsa kana ya bayar da dama a gudanar bincike.

Sai dai a maimakon ya amsa kiran da ake masa na ya sauka daga kan mukaminsa,Ganduje ya kai kara gaban kotu inda ya zargi jaridar Daily Nigerian da mawallafinta Ja’afar Ja’afar da zubar masa da mutunci da kuma bata masa ya kuma nemi da abiya shi diyar zunzurutun kudi biliyan ₦3.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]