Ganduje ya halarci bikin Mauludi a fadar Sarkin Kano

Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya jagoranci wata tawaga ta manyan jami’an gwamnati ya zuwa wurin Maulidi da aka gudanar a fadar mai martaba sarkin Kano Muhammad Sunusi II.

Shugaban darikar Kadiriya na Afrika ,Shekh Karibulla Nasiru Kabara shine yake jagoran maulidin da aka saba gudanarwa duk shekara.

Ziyarar ta daren Litinin na zuwa ne lokacin da gwamnan ke cigaba da fuskantar suka daga ciki da wajen jihar biyo bayan fefan bidiyon da wata jarida ta wallafa inda aka nuna shi yana karbar kudi daga hannun yan kwangila.

Mutane da dama dai nakira da gwamnan kan ya sauka daga kan mukaminsa kana ya bayar da dama a gudanar bincike.

Sai dai a maimakon ya amsa kiran da ake masa na ya sauka daga kan mukaminsa,Ganduje ya kai kara gaban kotu inda ya zargi jaridar Daily Nigerian da mawallafinta Ja’afar Ja’afar da zubar masa da mutunci da kuma bata masa ya kuma nemi da abiya shi diyar zunzurutun kudi biliyan ₦3.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]