Ganduje bai damu da binciken bidiyon dala ba—Tsohon Kwamishina

Muhammad Garuba, tsohon kwamishinan yada labarai na jihar Kano a karkashin gwamnatin Abdullahi Umar Ganduje ya ce tsohon gwamnan bai damu da matakin da gwamnatin jihar ta dauka na sake bude binciken faifan bidiyon dala da ke nuna yana karbar cin hanci ba.

Shugaban hukumar korafe-korafen jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano Barista Muhuyi Magajin Rimin-Gado, ya yi alkawarin sake bude binciken da ake yi wa tsohon gwamnan.

Rimin-Gado ya ce “Kowane gwamna, mataimakin gwamna ko shugaban kasa mai ci yana da kariya, yanzu wannan kariya ta kare, hukumar za ta yi abin da ya kamata.”

Sai dai tsohon kwamishinan yada labarai na jihar, Muhammad Garba, wanda abokin tsohon gwamnan ne, ya bayyana rashin damuwarsu game da lamarin a wata hira da BBC Hausa.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]