Dubban mutane a ƙasar Philippines sun tsere daga gidajensu bayan wani dutse mai aman wuta ya fara fitar da toka mai yawa a yankin.
Rahotanni sun ce dutsen Mayon da ke yankin Bicol ya yi aman wutar ne a ranar Asabar da ta gabata, inda ya fitar da toka da ta mamaye sararin samaniya.
Akalla mutane fiye da dubu biyar da ke zaune a kusa da dutsen sun tsere zuwa matsugunan gaggawa na wucin gadi, yayin da hukumomi ke ƙoƙarin share hanyoyin da toka ta rufe.
Philippines na daga cikin ƙasashen da ke yawan fuskantar bala’o’i a duniya, musamman aman wuta, girgizar ƙasa, ambaliya da kuma zabtarewar ƙasa.
Dubban Mutane Sun Tsere Sakamakon Aman Wutar Dutsen Mayon A Philippines

