Coronavirus: Buhari ya sassauta dokar kulle a Abuja, Legas, Ogun

Labari da dumi-dumi

—BBC Hausa

Shugaba Muahhamdu Buhari ya sassauta dokar kulle a jihohin Abuja da Legas da Ogun.

Sassaucin zai fara daga karfe 9:00 na safiyar Asabar 2 ga watan Mayu.

Ya ce: “Duba da wannan da kuma shawarwarin kwamitin fadar shugaban kasa na musamman da ke yaki da korona da kungiyar gwamnoni, na bayar da umarnin sassauta matakan kulle a Abuja da Legas da Ogun daga ranar Asabar 2 ga watan Mayun 2020 daga karfe 9 na safe.

“Burinmu shi ne mu samar da tsari da zai tabbatar da cewa tattalin arzikinmu ya ci gaba da aiki a yayin da a hannu guda kuma za ku ci gaba da daukar tsauraran matakai kan yaki da annobar cutar korona. “Wadannan matakai irin su ne shugabannin kasashe suka dauka a fading duniya.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]