Buhari ya sa baki kan batun Zainab Aliyu | BBC Hausa

Muhammadu Buhari

Hakkin mallakar hoto
Nigeria Presidency

Image caption

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya umarci Ministan Shari’a Abubakar Malami da ya shiga maganar Zainab Aliyu, ‘yar Najeriyar nan da ke tsare a kasar Saudiyya.

Jami’an tsaron Saudiyya sun kama Zainab Aliyu ne jim kadan bayan sun isa Saudiyya don yin aikin Umara ita da mahaifiyarta Maryam da kuma ‘yar uwarta Hajara.

Sun zarge ta da safarar kwayar Tramadol har guda 2,000 bayan da aka ga kwayoyin a wata jaka mai dauke da sunanta.

Amma tuni hukumar yaki da ta’ammali da miyagun kwayoyi ta NDLEA ta bayyana cewa wasu ma’aikata ne a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano (MAKIA) ne suka saka mata kwayar a jakarta.

Kwamandan hukumar mai kula da MAKIA Ambrose Omorou ya tabbatar wa da BBC cewa tuni suka kama mutum shida, wadanda ake zargi da aikata hakan.

Uku daga cikinsu ma’aikata ne da ke tantance kayayyakin matafiya, daya ma’aikacin wani kamfanin sufurin jirgin sama ne, sauran biyun kuma jmai’an tsaro ne a filin jirgin saman.

Kamar yadda ta wallafa a shafinta na Twitter, Abike Dabiri-Erewa mataimakiya ta musamman ga Shugaba Buhari kan harkokin kasashen waje ta ce shugaban ya umarci Abubakar Malami da ya shiga maganar.

“Buhari ya umarci ministan shari’a da ya yi dukkanin mai yiwuwa don ganin an yi wa Zainab adalci. Mahaifinta ne ya sanar da mu kuma muna samun ci gaba game da ita da sauran mutum biyun,” kamar yadda Abike Dabiri ta bayyana.

Wannan ya biyo bayan maganar da Sanata Shehu Sani ya yi ne, inda yake shawartar iyayen Zainab da su kawo kokensu gaban majalisar dokokin kasar domin ta shiga lamarin.

Dabiri ta kuma shaida wa jaridar Premium Times cewa Buhari ya shiga lamarin a lokacin da ya samu labari mako biyu da suka gabata.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa É—aya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faÉ—a tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...