Kungiyar Jama’at ahal as-Sunnah lid-Da’wah wal-jihad wanda aka fi sani da Boko Haram ta bayyana mamakin ta kan yadda wani mai sanya ido kan abubuwan dake faruwa a yankin arewa maso yammacin Najeriya ya samu labarin kisan wasu mambobin ta.
Mutumin da ake kira Zagazola Makama ya wallafa cewa cikin mutane 14 da aka kashe har da manyan kwamandodin kungiyar da suka kada da Abu Hassan.
Kungiyar ta ji labarin kisan ne a kafafen radiyo.
A cikin wani sako da ya wallafa Zagazola ya ce kungiyar na tunani yana amfani da wasu na’urori wajen yi musu leken asiri.
Ya kara da cewa kungiyar ta kuma fara zargin ko akwai yan leken asiri a cikinsu.