Ba mu kama Yari saboda ya ƙi ɗaukan kiran wayar Tinubu ba—DSS

A yau Lahadin ne jami’an farin kaya na DSS suka musanta cewa sun kama Sanata Abdulaziz Yari ne saboda ya ki amsa kiran wayar shugaban kasa Bola Tinubu.

Kakakin hukumar DSS, Dr Peter Afunanya, ya bayyana haka ne a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi.

Sanarwar da aka wallafa a shafin Twitter na hukumar ta DSS ta bayyana ikirarin a matsayin abin dariya

Da yake tabbatar da cewa DSS ne ta gayyaci Yari, Afunanya a cikin sanarwar ya ce Sanatan ya san dalilin gayyatar sa.

Ya kuma musanta zargin da ake yi wa hukumar na yi wa alkalan kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa zagon kasa.

More News

Gwamnatin Adamawa Ta Ƙara Hutun Ɗaliban Makarantu Saboda Annobar Cutar Ƙyanda

Gwamnatin jihar Adamawa ta tsawaita lokacin komawar ɗaliban jihar makarantunsu domin fara  zangon karatu na uku saboda annobar cutar ƙyanda. A wata sanarwa ranar Litinin,...

Sojan Jamhuriyar Nijar sun kama Gawurtaccen Ɗan Fashin dajin Najeriya Kachalla Mai Daji

Dakarun sojan Jamhuriyar Nijar sun samu nasara kama gawurtaccen ɗan fashin dajin nan mai suna Kachalla Mai Daji a garin Illela dake kan iyakar...

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraɗiyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...