Ba mu kama Yari saboda ya ƙi ɗaukan kiran wayar Tinubu ba—DSS

A yau Lahadin ne jami’an farin kaya na DSS suka musanta cewa sun kama Sanata Abdulaziz Yari ne saboda ya ki amsa kiran wayar shugaban kasa Bola Tinubu.

Kakakin hukumar DSS, Dr Peter Afunanya, ya bayyana haka ne a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi.

Sanarwar da aka wallafa a shafin Twitter na hukumar ta DSS ta bayyana ikirarin a matsayin abin dariya

Da yake tabbatar da cewa DSS ne ta gayyaci Yari, Afunanya a cikin sanarwar ya ce Sanatan ya san dalilin gayyatar sa.

Ya kuma musanta zargin da ake yi wa hukumar na yi wa alkalan kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa zagon kasa.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]