Aston Villa za ta bai wa Steven Gerard aikin koci

Steven Gerard

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto,
Steven Gerrard, ya karbi aikin horar da Rangers a 2018 ya lashe Liik din kasar a karon farko tun bayan shekara 10

Kocin Rangers, Steven Gerrard ya na daga cikin wanda Aston Villa ke son dauka, domin maye gurbin Dean Smith, wanda ta kora.

To sai dai kuma kungiyar na tuntubar wasu masu horar da tamaula koda Gerard ba zai amince da tayin da aka yi masa ba.

Mahukuntan Villa sun gamsu da aikin da Gerard ke gabatarwa a Rangers a karon farko da ya fara aikin horar da kwallon kafa.

Ana alakanta shi da cewar shine zai zama kocin Liverpool na nan gaba da zarar Jurgen Klopp ya ajiye aiki a Anfield.

Gerard mai shekara 41 yana da kyakkyawar alaka da babban jami’in Villa kuma tsohon kocin Rangers, Christian Purslow.

Villa na neman kocin da zai dora inda Smith ya tsaya, wadda za ta buga wasan gaba a Premier League da Brighton ranar 20 ga watan Satumba.

Ana alakanta aikin da kociyan tawagar Belgium, Roberto Martinez da na Denmark, Kasper Hjulmand.

Ana kuma cewar Villa tana sha’awar daukar mai horar da Southampton, Ralph Hasenhuttl da na Brighton, Graham Potter.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...