Pep Guardiola ya sa hannu kan yarjejeniyar shekara biyu, domin ci gaba da horar da Manchester City zuwa karshen kakar 2023.
Mai shekara 49 ya lashe kofin Premier League biyu da FA Cup da League Cup uku, tun lokacin da ya koma kungiyar a 2016.
Tun farko kwantiragin tsohon kocin Barcelona da Bayern Munich zai kare ne a karshen kakar tamaula ta bana.
Shekara biyar da Guardiola ya yi a City, ita ce kungiyar da ya dade yana jan ragama tun bayan da ya zama kocin tamaula a 2008.
Idan Guardiola ya kammala yarjejeniyarsa a kungiyar zai zama na biyu da ya dade a Manchester City, matakin da Joe Mercer ke kai a yanzu.
Wanda yake na daya da ya dade yana horar da City shi ne Les McDowall, wanda ya ja ragamar wasa 592 tsakanin 1950 da kuma 1963.
Kawo yanzu da Guardiola ke aikin horar da City, kungiyar ta yi nasara a wasa 181 daga 245 da ta fafata, wato ya yi nasara kaso 73.87 cikin 100 kenan.
(BBC Hausa)