Real Madrid za ta yi wasan sada zumunta da Rangers

Carlo Ancelotti

Asalin hoton, Getty Images

Real Madrid za ta ziyarci Glasgow, domin buga wasan sada zumunta da Rangers ranar 25 ga watan Yuli.

Shine wasan farko da Carlo Ancelotti zai ja ragamar Real Madrid a karo na biyu da zai horar da kungiyar.

Real din za ta kara da Rangers wadda ta lashe kofin gasar Scotland a kakar da ta kare tare, wadda tsohon dan wasan Liverpool, Steven Gerrard ke kocinta.

Real Madrid za ta yi wasan sada zumunta biyu ko uku, don shirin tunkarar kakar bana ta 2021/21, wadda za ta fara karawar farko da Alaves a La Liga ranar 14 ga watan Agusta.

Wasan karshe da kungiyoyin suka kara shine wanda Real Madrid ta doke Rangers 7-0 a European Cup.

Gerrard zai ja ragamar kungiyar wasan cike gurbin shiga gasar Champions, sakamakon da Rangers ta lashe kofin gasar Scotland a kakar da aka karkare.

More News

Kotu ta É—aure mutumin sa ya yi sama-da-faÉ—i da kuÉ—in marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...

NFF ta naÉ—a Finidi George a matsayin sabon kocin Super Eagle

An naɗa Finidi George a matsayin sabon mai horar da kungiyar ƙwallon ƙafar Najeriya wato Super Eagle. Hukumar ƙwallon Ƙafa ta Najeriya, NFF ita ta...

Gwamnan Edo Zai Fara Biyan 70,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki ya sanar da mafi ƙarancin albashi ga ma'aikatan ga ma'aikatan jihar inda za a riƙa biyan naira dubu 70,000. Gwamnan...

JAMB ta fitar da sakamakon jarabawar 2024

Hukumar shirya jarabawar shiga makarantun gaba da sakandire ta JAMB, ta fitar da sakamakon jarrabawar shekarar 2024, watau sakamakon UTME.Sama da mutane miliyan 1.94...