APC ta Nada Abiola Ajimobi a Matsayin Mukaddashin Shugabanta | VOA Hausa

Kotun daukaka kara ta Najeriya ta tabbatar da dakatarwar da a ka yi wa shugaban jam’iyyar APC Adams Oshiomhole daga kujerarsa.

Dama babbar kotun da ke Abuja ta dakatar da shi daga kujerar a watan Maris na wannan shekarar ta 2020, biyo bayan karar da wasu masu ruwa da tsaki a jam’iyyar suka shigar, ciki har da shugaban ta na arewa maso gabas Kwamred Mustapha Salihu.

Adams Oshiomhole ya daukaka kara bayan da aka hana shi shiga ofishin helkwatar jam’iyyar da ke unguwar Wuse 2 a Abuja.

Yanzu dai an zuba ido a ga yiwuwar daukaka kara daga Adams Oshiomhole zuwa kotun koli da kuma yadda jagorancin jam’iyyar zai kasance bayan wannan hukunci.

Alkalan kotun daukaka karar a karkashin jagorancin Jostis Monica Dongban-Mensen ne su ka yanke hukuncin suna mai cewa daukaka karar dakatarwar ta Oshiomhole ba ta da ma’ana ko hujja.

Wannan sabuwar dakatarwar ta zo ne a tsakiyar dambarwar da ke faruwa a jam’iyyar APC da gwamnan jihar Edo Godwin Obaseki bayan da aka hana gwamnan damar tsayawa takara.

Tuni dai jam’iyyar ta APC ta nada mataimakin shugaban jam’iyyar na kudancin Najeriya Abiola Ajimobi a matsayin mukaddashin shugabanta.

Ko da ya ke, sakataren walwalar jam’iyyar Ibrahim Masari, ya bayyana wa Muryar Amurka yadda kundin tsarin jam’iyyar ya tsara nada mukaddashi a irin wannan yanayi ya kuma ce za su daukaka kara zuwa kotun koli.

More News

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...

Delta: An dawo da gawarwakin sojojin da aka kashe Abuja don yi musu jana’iza

Gawarwakin sojojin da aka kashe a jihar Delta kwanan nan sun isa maƙabartar sojoji ta kasa da ke Abuja. Gawarwakin sun iso ne da misalin...