Ana fargabar mutuwar mutane 40 a wani haɗarin jirgin ruwa a jihar Sokoto

Sulaiman SaadArewaMoreHausa27 minutes ago

Aƙalla mutane 40 ake fargabar sun mutu bayan da jirgin kwale-kwale da suke ciki ya nutse a kauyen Gorau dake ƙaramar hukumar Goronyo ta jihar Sokoto.

A cewar jaridar Punch lamarin ya faru ne a ranar Alhamis lokacin da jirgin kwale-kwalen dake ɗauke da fasanjoji 40 ciki har da maza, mata da kuma ƙananan yara ya kife  da su a cikin ruwa.

Kawo yanzu babu haƙiƙanin adadin mutanen da su ka mutu saboda jami’ai na can na cigaba da gudanar da aikin ceto har ya zuwa dai-dai lokacin da aka wallafa labarin.

Kokarin da aka yi na jin ta bakin mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Sokoto, Ahmad Rufa’i.

Jihar Sokoto dai na daga cikin jihohin da ake yawan samun hatsarin jirgin kwale-kwale a  Najeriya musamman a irin wannan lokaci da ake ciki na damuna

t

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...