An yi waje da Man United a Champions League na bana

RB Leipzig

Manchester United ta yi rashin nasara da ci 3-2 a gidan RB Leipzig a gasar Champions League ranar Talata a Jamus.

Cikin minti 13 aka zura kwallo biyu a ragar United ta hannun Angelino da kuma Amadou Haidara.

A minti na 69 ne Justin Kluivert ya kara kwallo na uku a ragar Manchester United.

Sai a min 80 United ta fara sa kwazo ta zare kwallo daya ta hannun Bruno Fernandes a bugun fenariti, kuma minti biyu tsakani Paul Pogba ya zare na biyu.

United wadda ya kamata ta yi canjaras domin zuwa mataki na biyu ta koma ta uku a cikin rukuni da maki tara.

RB Leipzig ce ta zama ta daya a rukunin na takwas da maki 12.

Kungiyar ta Old Trafford za ta koma buga gasar Europa League, kofin da ta lashe a kakar 2017.

More News

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...

An fara rushe wasu gine-gine 500 a kasuwar Karmo dake Abuja

Hukumar FCTA dake kula da birnin tarayya Abuja ta fara rushe gine-gine sama da 500 da aka yi ba bisa ka'ida ba a kasuwar...

Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa

A ranar Alhamis ne shugaba Bola Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa, a ziyarar da Faye ya...

NEMA ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo dasu gida daga ƙasar Chad

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA ta ce ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo da su bayan da su ka maƙale...