An Yi Awon Gaba Da Basarake A Jihar Kogi

Wasu mahara sun sace Sarkin Aghara a karamar hukumar Kabba-Bunu da ke jihar Kogi a tsakiyar arewacin Najeriya.

Jaridar Daily Trust da ta ruwaito labarin ta ce an kashe wata mata a fadar Sarki Pa David Obadofin yayin harin da ‘yan bindigar suka kai da sanyin safiyar Talata.

Baya ga Pa Obadofin da suka sace, ‘yan bindigar har ila yau sun yi garkuwa da wasu manyan fadawa biyu.

Bayanai sun yi nuni da cewa maharan sun fada farfajiyar fadar ne suna harbin kan mai uwa da wabi a lokacin da suka kai harin.

Rundunar ‘yan sanda jihar ta Kogi ta tabbatar da aukuwar lamarin tana mai cewa ta tura jami’anta don kubutar da mutanen tare da kama ‘yan bindigar.

More News

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

Sojoji sun gano masana’antar Æ™era bom a jihar Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya sun gano wata masana'anta da mayaƙan kungiyar ISWAP suke ƙera bama-bamai. Masana'antar ƙera bama-bamai an gano ta ne a Abulam-BUK dake...

Atiku ya ziyarci Abdul Ningi

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya ziyarci dakataccen ɗan majalisar dattawa sanata, Abdul Ningi dake wakiltar mazaɓar Bauchi ta tsakiya a majalisar dattawa. Atiku...