An Kori Ƴan Sandan Dake Bawa Rarara Kariya Daga Aiki

Rundunar yan sandan Najeriya ta kori jami’an ta uku bayan da ta same su da saɓawa dokokin aikin rundunar.

Jami’an da aka kora sune ke bada kariya ga shahararren mawakin nan Dauda Adamu Abdullahi Rarara

Yan sandan sun fito ne daga runduna ta musamman dake bawa muhimman mutane kariya.

A kwanakin baya ne wani fefen bidiyo ya bayyana a kafafen sada zumunta da ya nuna yan sandan na harbi sama lokacin da suka raka shahararren mawakin garinsu na Kahutu dake jihar Katsina.

Yan sandan da aka kora sun haɗa da Insifecta Dahiru Shuaibu, Sajan Isa Danladi da kuma Sajan Abdullahi Badamasi.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]