An fassara wasu littafan PHYSICS, CHEMISTRY, MATHEMATICS zuwa HAUSA

Photo credit: arewagist.com

Cibiyar Bincike Kan Harsunan Nigeria da Fassara da Hikimomin Al’umma tabJami’ar Bayero, Kano ta yi nasarar fassarawa tare da wallafa litattafan kimiyya guda takwas zuwa harshen Hausa saboda daliban Piramare, Karamar Sakandare (Junior) da kuma babbar Sakandare (Senior) Saboda dalibai ‘yan yankin Arewacin Najeriya.

Farfesa Aliyu Mu’azu, daraktan wannan cibiyar ya ce, “litattafan da aka fassara su ne:
1. Kimiyya da Fasaha don makarantun Firamare. Littafi na daya zuwa na uku.
2. Lissafi don Kananan makarantun Sakandare. Littafi na daya zuwa na uku.
3. Kyamistare (Chemistry) don manyan makarantun Sakandare.
4. Fizis (Physics) don manyan makarantun Sakandare.
Haka kuma wajen yin aikin wannan fassara Farfesa Mu’azu yace sunyi amfani ne da tsarin karantarwa na kasa (National Curriculum) tare da Taimakon abokan aikin su na Faculty of Science da kuma Faculty Of Education.
Farfesa Mu’azu yace “Shawarar fassara wadannan Litattafan da kuma buga su yazo ne sakamakon kokarin da wannan cibiya takeyi na ganin ta bada nata gudun muwa wajen habaka ilimin zamani a yankin mu na Arewa ta hanyar koyarda ilimin da harshen uwa (Yaren mu/Hausa) dan haka wannan cibiya tayi amannar cewa koyo da koyarwa zai kasance mafi sauki da kuma fahimta matukar dai anayi ne da harshen Hausa (Mothers tongue) hakanan ya kara da cewa kaje kasashen da suka cigaba kagani, zakaga sirrin cigaban ilimin su shine koyar da shi da sukeyi da yaren su. A karshe Farfesa Mu’azu yace ” Cibiyar zatayi kokari wajen hada kai da hukumomin Jahohi dana tarayya dan tabbatar da cewa wadannan Litattafan ana amfani dasu a makarantun kasar”
A jawabin sa mataimakin Shugaban Jami’ar Farfesa Muhammmad Yahuza Bello yace “Yayi alkawarin taimakawa duk wani cigaba da wannan cibiya ta kawo don habaka yaren Hausa (Mothers tongue) a arewacin Nigeria dama kasa baki daya. Haka kuma ya yabawa wannan Cibiya bisa wannan namijin kokari da tayi, yace wannan cigaba ne bawai ga Cibiyar kawai ba, har dama Jami’ar ta Bayero baki daya”
Itama a nata Bangaren Kungiyar Arewa Students Orientation Forum ta yabawa wannan cibiya bisa wannan Namijin Kokarin, kazalika daman Kungiyar tayita kiraye-kiraye akan yin wannan aikin na fassara, gashi Alhamdu_Lillah an fara samun Nasara. A karshe Kungiyar ta Arewa SOF tana kira ga daukacin hukumomin Jahohi dana tarayya da su amince da yin amfani da wadannan Litattafan a makarantun mu, dan haifar da kwararrun likitoci, injiniyoyi, da Sauran su.

More News

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Gidaje 8925

Gwamnatin tarayya ta ce ta fara raba gidaje 8925  ga mutanen da suka nema kuma suka cancanci a basu a faɗin ƙasa baki ɗaya...

Ƴan Bindiga A Zamfara Sun Kashe Sakataren Jam’iyar PDP

Wasu ƴan bindiga da ba a san ko suwaye ba sun kashe, Musa Ille  sakataren jam'iyar PDP na ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara. Zagazola...