An Bukaci Kotu Ta Dakatar Da Rantsar Da Shugaba Buhari | VOA Hausa

A wata rubutaciyar takardar jawabi da Jamiyar Hope Democratic Party ta raba wa manema labarai na nuni da cewa sun shigar da karar ne a bisa wasu dalilai da dama, amma muhinmi dalili shi ne cewa akwai wata shari’a da aka riga aka shigar dake kalubalantar nasarar da shugaba Mohammadu Buhari ya samu a zaben da aka gudanar a ranar 23 ga watan Fabrairu na wanan shekara.

Wani kwararre a bitar kundin tsarin mulki Barista Mainasara Kogo Ibrahim ya yi fashin baki a kan ko Jamiyar Hope Democratic Party tana da hurumin shigar da irin wannan kara bayan an kammala shirye-shiryen rantsar da shugaban kasar. Barrister Mainasara ya ce zata iya shigar da kara amma kuma matakin zai haifar da rudani.

A nashi jawabi, tsohon shugaban hukumar wayar da kan al’umma ta Kasa Dokta Mike Omeri ya ce duka da cewa Jamiyar Jamiyar Hope Democratic Party tana da hurumin shigar da kara amma a yi taka tsantsan saboda duk abin da kotu zata yi, a bi abin da dokar kasa ta tanada domin kada a jefa kasa a cikin wani halin kakanakayi.

Jamiyar Jamiyar Hope Democratic Party ta ce an riga an kaiwa shugaba Buhari takardar karan dake bayanin cewa in har an dasa ayar tambaya a wajen Kalubalantar zaben nasa, toh bai cancanci daukar rantsuwa ba.

Sai dai a daidai lokacin daukan wanan rahoto fadar shugaban kasa ba ta mayar da martani ba.

More News

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraÉ—iyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...