An karrama Ali Nuhu a Indiya | Arewa News

An karrama tauraron finafinan Hausa Ali Nuhu a Indiya, kamar yadda ya bayyana wa BBC.

Wasu ɗalibai ‘yan Arewacin Najeriya da ke karatu a ƙasar Indiya da malaman su Indiyawa ne su ka gayyaci jarumin bikin Ranar Al’adu kuma su ka karrama shi a wajen taron.

“Ɗaliban na karanta fanni daban-daban, kama daga fannin likita zuwa haɗa magunguna da injiniya da dai sauransu,” inji Ali Nuhu.

Jarumin ya ce baya ga waɗannan ɗalibai, wasu makarantu a ƙasar sun ba shi lambobin yabo.

Ali Nuhu ya ce, “Akwai makarantar MVM Group of Instututions, su ma sun ba ni lambar yabo kuma sun nuna jin daɗin su kan yadda ɗaliban Najeriya ke mayar da hankali kan karatunsu.”

Tauraron ya ce ya yi matuƙar farin ciki da wannan karramawa da kuma yadda malaman waɗannan makarantu ke da sha’awar al’adun Hausawa.

“Wasu daga cikin malaman har finafinan Hausa su ke kallo saboda su ga yadda yanayin rayuwar Bahaushe ta ke.

“Shi ya sa idan wani ɗan wasa ya zo taro irin wannan su kan karrama shi,” inji Ali Nuhu.

More News

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Gidaje 8925

Gwamnatin tarayya ta ce ta fara raba gidaje 8925  ga mutanen da suka nema kuma suka cancanci a basu a faɗin ƙasa baki ɗaya...

Ƴan Bindiga A Zamfara Sun Kashe Sakataren Jam’iyar PDP

Wasu ƴan bindiga da ba a san ko suwaye ba sun kashe, Musa Ille  sakataren jam'iyar PDP na ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara. Zagazola...