Abin da ya sa Man City ta doke mu – Mourinho

Manchester

City ta doke United da ci 3-1 – abin da ya sa ta hawa teburin gasar firimiya

Kocin Manchester United Jose Mourinho ya ce Manchester City ta yi galaba ne a kansu saboda yadda suka yi shiri sosai a wasu wasannin sada zumunta biyu da suka buga a makon da ya wuce.

Man City ta koma saman teburin gasar firimiya ne bayan David Silva da Sergio Aguero da kuma Ilkay Gundogan sun zura kwallo daya-daya kowannensu – abin da ya ba su maki uku a filin wasa na Etihad.

A ranar Lahadi ne City ta doke United da ci 3-1, abin da ya sa United din ta tsaya a mataki na takwas a teburin gasar.

Mourinho ya ce City ta samu galabar ce saboda sun doke Southampton da kuma Shakhtar Donetsk a gida inda suka ci kwallaye 12-1 jumulla.

Ya ce wadannan nasarorin sun fi wadda United ta samu tasiri, kafin karawarsu.

Wannan ne wasa na uku a jere ba a gida ba da United ta yi, biyo bayan doke Bournemouth a gida da waje a karshen makon jiya da kuma nasarar da ta samu a kan Juventus a ranar Laraba.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]