’Yan Sanda Sun Kama Boka Kan Zargin Wulaƙanta Alƙur’ani A Kebbi



Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kebbi ta kama wani mutum mai suna Abubakar Musa, mai shekaru 29, bisa zargin hannu wajen wulaƙanta Alƙur’ani da kuma wasu ayyukan da ake zargin na tsafi ne.

An kama Musa a ƙauyen Rafin Mose da ke Ƙaramar Hukumar Zuru, bayan da ’yan sanda suka fara bincike kan wasu abubuwa da aka gano an binne su a wani rami da aka haƙa a ɗakin wata mata mai suna Zara’u Hassan a unguwar Zango.

Kakakin rundunar, SP Bashir Usman, ya ce daga cikin abubuwan da aka gano akwai Alƙur’ani, goro fari da ja, tufafi, matattun dabbobi da wasu abubuwa da ake zargin na tsafi ne.

A cewar ’yan sandan, ana zargin mijin Zara’u, Rabi’u Tela, da wasu mutane biyu, Abubakar Musa da Hamza Zango, da haƙa ramin tare da binne abubuwan domin tilasta wa Zara’u biyayya ga mijinta.

Rundunar ta ce Rabi’u Tela da Hamza Zango sun tsere, yayin da Abubakar Musa ke hannun ’yan sanda. Za a gurfanar da shi a gaban kotu bayan kammala bincike.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Kebbi, CP Umar Haɗeja, ya yi Allah-wadai da lamarin, tare da tabbatar da cewa rundunar ba za ta lamunci duk wani abu da zai wulaƙanta addini ko kawo tashin hankali tsakanin jama’a ba.

Ya kuma buƙaci jama’a da su taimaka wa jami’an tsaro da bayanan da za su taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya a jihar.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...