Amurka Ta Kai Hare-Hare Kan Tashar Jiragen Ruwan Iran


Rahotanni daga Iran sun ce Amurka ta kai hare-haren makamai masu linzami a wasu wurare da ke ƙasar, ciki har da tashar jiragen ruwa ta Bandar Abbas da tsibirin Qeshm da ke gaɓar Tekun Fasha.

Gidan talabijin na gwamnatin Iran ya ce an ji ƙarar fashe-fashe a yankuna da dama, yayin da aka kuma kunna garkuwar sararin samaniya a babban birnin ƙasar, Tehran.

Hare-haren sun biyo bayan barazanar da Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi na hukunta Iran da ƙawayenta na Houthi da ke Yemen, saboda hare-haren da mayaƙan Houthi ke kai wa jiragen dakon man Saudiyya a Tekun Maliya.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]