Tsawa Ta Kashe Yara 6, Ta Jikkata 2 A Adamawa



Akalla yara 6 sun mutu, yayin da wasu 2 suka jikkata bayan tsawa ta same su a lokacin da suke aikin roron gyada a wata gona da ke jihar Adamawa.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne yayin da ake ruwan sama, lokacin da tsawa ta afku a yankin.

Masana sun ce ana yawan samun irin wannan hatsari a lokacin damina, inda suka bukaci jama’a su guji zama a fili ko karkashin bishiyoyi idan ana tsawa, tare da bin shawarwarin kariya domin rage haÉ—arin irin wannan lamari.

More from this stream

Recomended