Tsohon shugaban jam’iyyar APC na farko a Jihar Jigawa, Ado Sani Kiri, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar a hukumance.
Kiri, wanda ya wakilci mazabar Ringim/Taura a Majalisar Wakilai daga 2019 zuwa 2023, ya bayyana hakan ne a cikin wasiƙar murabus mai ɗauke da kwanan watan 30 ga Maris, 2026, wadda ya aika wa shugaban APC na gundumar Kiri, Malam Saliku Mujtapha.
A cikin wasiƙar da aka bai wa manema labarai a ranar Juma’a, ya ce ya ɗauki matakin ne bayan zurfin tunani da kuma yanke shawarar kansa na janyewa daga harkokin jam’iyya.
Ya kuma nuna godiyarsa ga jam’iyyar bisa damar da aka ba shi na bayar da gudunmawa wajen ci gabanta da harkokinta na siyasa.
Ficewar tasa na haifar da muhawara a tsakanin ‘yan siyasa a jihar, duba da rawar da ya taka a gina tubalin APC tun kafin zaɓen 2015 da kuma tasirinsa a harkokin siyasar jihar.
Sai dai bai bayyana ko yana shirin komawa wata jam’iyya ba, lamarin da ke haifar da hasashe kan matakin da zai ɗauka a gaba.
Tsohon Shugaban APC A Jigawa, Ado Kiri, Ya Fice Daga Jam’iyya

