Jamus Da Birtaniya Sun Kauracewa Shiga Yakin Iran

Gwamnatocin Jamus da Birtaniya sun bayyana cewa ba su ga wata rawa kai tsaye da za su taka ba a rikicin da ke gudana da Iran.

Jamus ta jaddada cewa rikicin ba shi da alaƙa da ƙungiyar tsaro ta NATO, inda ta ce ba za ta tura sojoji domin taimakawa wajen warware matsalar rufe mashigin Hormuz da Iran ta yi ba.

A nata bangaren, Firayim Ministan Birtaniya, Keir Starmer, ya ce gwamnatinsa ba ta son a jawo ta cikin wani sabon rikici a yankin Gabas ta Tsakiya.

Sai dai ya bayyana cewa Birtaniya na aiki tare da ƙawayenta domin samar da hanyoyin da za su tabbatar da buɗe mashigin.

“Wajibi ne mu sake buɗe mashigin Hormuz, domin samar da daidaito a kasuwar man fetir ta duniya, wannan ba abu ne mai sauƙi ba,” in ji Kier Stermer.

Tun da farko, tsohon shugaban Amurka Donald Trump ya yi gargadi cewa ƙasashen NATO za su fuskanci sakamako mara kyau idan suka ƙi bayar da gudunmawa wajen shawo kan lamarin.

More from this stream

Recomended