Rahotanni sun bayyana cewa an ji fashe-fashe tare da tashin hayaki a Tehran, babban birnin Iran, a daidai lokacin da Isra’ila ta ce tana ƙara faɗaɗa hare-haren da take kai wa.
A nata ɓangaren, Iran ta ce tana ci gaba da kai hare-haren ramuwar gayya a biranen Tel Aviv da Jerussalam da sauran yankunan Isra’ila.
Rikicin na ƙara tsananta a yankin Gabas ta Tsakiya, inda Iran ta ce hare-haren da take kaiwa suna nufin muradan Amurka ne, ba ƙasashen maƙwabta ba.
A wani ci gaba, an sake rufe filin jirgin sama na Dubai bayan wani harin jirgin sama maras matuƙi da ya haddasa gobara a wani tankin mai da ke kusa.
Haka kuma a Iraqi, jami’ai sun tabbatar da cewa mutum biyar sun jikkata sakamakon harin roka da aka kai filin jirgin sama na Baghdad, inda ofishin jakadancin Amurka yake.
Shugaban Amurka Donald Trump ya sake bayyana cewa ana tattaunawa da jami’an Iran. Sai dai ministan harkokin wajen Iran ya musanta wannan ikirari, kamar yadda aka saba gani a baya, abin da wasu masana ke dangantawa da gajiya da yaƙin da Amurka ke fuskanta.
Fashe-Fashe Sun Auku A Tehran Yayin Da Rikici Tsakanin Iran Da Isra’ila Ke Ƙaruwa

